8.11.07

MAFARKIN SHABBAKIN MANZON ALLAH SAWA

KIN MANZON SALAM.
Bayan haka ina yiwa al'ummar musulmi masoya Manzo Muhammad SAWA da Iyalansa tsarkaka a duk inda suke a duniya fatan alheri, musamman 'yan uwana 'yan darikar Tijjaniyya ta Maulanmu Shehu Ahmad Tijjani RTA da kuma masoyanmu masu kaunarmu a duk inda suke.
Bayan haka yau Litinin 26-10-1428 (5-11-2007) da daddare da misalin karfe 2:00 na dare ina barci sai nayi mafarki da Shabbakin Manzon Allah SAWA da yake garin Madina, inda na ganni a bakin Shabbakin a tsaye wasu mutane fararen fata suna zuwa domin suyi ziyara ga Manzon Allah SAWA ana korarsu idan suna yin addu'o'i a wajen, inda shi mai kula da wajen wanda bakar fata ne kuma yana magana da harshen Hausa, yake nuna mini wadannan mutane suna yin wani abu ne mara kyau, a halin ba abin da suke yi sai tawassilli da Manzon Allah SAWA. A lokacin dana kusancin makwancin Manzon Allah SAWA sai na leka ta wata kofa inda naga Kabarinsa mai albarka da kwarjini, sannan a gefen kabarin akwai wasu kabararruka kana guda uku wanda basu kai na Manzon Allah SAWA girma ba, su wadannan kananan kabararruka sai na ga shi wannan mutumi mai kula da wajen yana diban wasu sarkoki na gwalagwalai yana yi musu ado da su amma bai kula da na Manzon Rahama SAWA ba. A lokacin da nake leka kabarin Manzon Allah SAWA ta cikin wasu kananan kofofi sai nake fadin,"ASSALATU WASSALAMU ALAIKA YA MUHAMMADUR RASULILLAH ! ASSALATU WASSALAMU ALAIKA YA ABUL FATIMA ZAHARA'U ! ASSALATU WASSALAMU ALAIKA YA ABUL KASIM ! ASSALATU WASSALAMU ALAIKA YA ABUL ZAINAB ! ASSALATU WASSALAMU ALAIKA YA ABUL UMMUL KULSUM!..... ......... ."
Haka na ganni ina ta yiwa Manzon Allah SAWA kirari da salati, har sai dana ga kabarinsa yana dada girma yana yin numfashi kamar kabarin zai bude ya fito. A lokacin da wannan mai kula da kabarin ya ga halin da nake ciki wanda har na fita daga hayyacina saboda kirarin da salati da nake yi masa SAWA a gaban kabarinsa SAWA, sai wannan mai kula da waje ya kama ni ya damkawa wani askari ni, wato sojan kasar Saudiya, wanda shi kuma ya rike hannayena guda biyu ya tafi dani wajen shugabansa wanda shi kuma ya umarce shi daya kai ni wani waje da suke azabtar da mutane. A lokacin sai wannan soja yake duka na da wani abu mai kama da bindiga, amma sai nake ji kamar yana shafata da wani abu mai tsananin taushi banji alamar wani ciwo ko zafi ba.
A lokacin da wannan askari yake kokarin tafiya dani sai nake masa magana da harshen turanci al'amarin daya jawo dimbin jama'ar da suke zaune a cikin masallacin suka saurari tambayar da nake yiwa wannan askari, kuma suka zaku su ji tambayar da nake yi masa da amsar da zai bani.
Na tambayi wannan askarin cikin harshen turanci shin bani da iko in bi mazahabar da nake ganin itace ta dace na bita, kuma na aiwatar da ayyukan ibadata daidai da fahimta ta?
A lokacin da nake tambayar wannan askarin sai yake kokarin ya hana ni karasa tambayata saboda ya hana mutane su fahimci wane ne mai gaskiya a tsakani na da shi, inda yake fada mini wai limaminsu Sudais ma'asumi ne don haka kawai in bi hanyar limamansu.
A lokacin da wannan askari ya gaza hana jama'a fahimtar abin da nake son fada har jama'a suka fahimci abin da yake faruwa sai kawai naga jama'a bakaken fata da suke wajen wanda akasarinsu talakawa ne masu kananan sana'o'i irin sai da lemon zaki, sun watsar da kayan sana'arsu sun nufo inda nake, suma mata wanda na gansu cikin shiga irin ta matan 'yan uwa musulmi almajiran Malam Zakzaky sanye da hijabi wanda suma suka baro wajen da suke a zaune a masallacin suka nufo inda nake inda na gansu dubunnai suna fadin, "ASSALATU WASSALAMU ALAIKA YA MUHAMMADUR RASULILLAH ! ASSALATU WASSALAMU ALAIKA YA MUHAMMADUR RASULILLAH !!"
Wannan askar da sauran 'yan uwansa suna ganin yadda mutanen nan suka kawo mini tallafi sai ya sake ni ya nemi sulhu dani.

Wannan shine mafarkina wanda nayi kuma dama wani abu makamancin haka ya taba faruwa da ni a lokacin dana je aikin Hajji a shekarar 2000.
Allah ya kara mana son Manzon Allah SAWA da Iyalansa tsarkaka da masoyansu ko da kuwa muna da bambamcin fahimta dasu matukar dai su masoyan Manzon Manzon Allah SAWA ne da Iyalansa tsarkaka.
Wannan mafarki nawa yana dauke da babban sako ga mai hankali.
Daga,
Rabiu Yusuf Kano,

SUN FI SU

A sakamakon mukalar dana aikowa da mujallar Fim mai farin jini wadda na bayyana cewa 'yan fim sun fi malamai masu kasuwanci da ayoyin Allah SWT fadakarwa wadda mujallar fim ta buga, na samu kiran waya da sakonni daga jihohi da dama da suke kasar nan ta (Najeriya). Babu lokacin da zan bayyana irin sakonnin dana samu daga wajen Malamai da matasa sai dai in ce lalle ina kara jaddada maganata cewa 'Yan Fim sun fi Malamai Fadakarwa amma fa Malamai masu boye gaskiya suna bayyana karya da son zukatansu, Malamai masu kafirta al'ummar Muhammadu Rasulillahi SAWA saboda kawai ba sa bin abin da suke so na zalunci da son zukatansu.
Shin mai yiwa Allah SWT da Manzonsa SAWA karya ne yafi zalunci ko kuwa wanda yake rawa da matar da bata sa ba? Kuma al'umma kun san wanda ya kirkiri karya ya jinginawa Allah SWT da Manzonsa SAWA don biyan bukatarsa kansa ko bukatar ubangidansa yafi zalunci akan wanda ya ke rawa da waka da matar da ba muharramar sa ba.
Ina so al'umma ta fahimci sai bango ya tsage kadangare yake samun wajen shiga ya fake, ma'ana sai Malamai sun zama masu kwadayi da karya da yaudara sannan al'umma take lalacewa. Abin daya faru kwanan nan ga 'yar uwata musulma MARYAM USMAN HIYANA ba kowa ya bada kofar faruwar hakan ba face malamai domin su ne basu yi aikin da Allah SWT ya dora musu ba saboda tsoron dauri da talauci. Lalle da Malamai sun fadakar sun tsoratar da al'umma tun farkon bayyanar Fim din SANGAYA wanda shine ya jawo matasa maza da mata suka bazama neman shiga harkar Fim don su ma duniya ta san su, su yi suna, su nuna irin halittar da Allah SWT yayi musu ga masu bukata, da wancan al'amarin rashin jin dadi bai faru ga waccan matata ba.
Ina son masu karatu da wanda suka kira ni a waya su sani cewa ni bana tsoron mutuwa akan gaskiya domin ita mutuwa dole ce, wani ma ya yadda ya mutu a hanyar kafirci bare ni da nake kira a bi hanyar gaskiya hanyar Allah SWT. Bana kaunar abin da Malaman mu suka jawo mana na kaskanci wanda yayi sanadin 'yan mata musulmi suka gwammace shiga harkar fina-finan hausa maimakon yin aure wanda shine yafi mutunci a gare su da mu kan mu. Malamai da kun jefar da al'adar kafirta musulmi mai salla da azumi da zikirin Allah SWT kun bi hanyar da Muhammadu Dan Abdullahi, Baban Sayyada Fatima, Yayan Aliyu Dan Abi Dalib, Kakan Hassan da Hussain da Shehu Tijjani da Sidi Abdulkadir Jilani, tsiran Allah da albarka su kara tabbata ga shugabana Muhammad da Iyalansa masu tsarki, wallahi Allah da babu wata yarinya baliga musulma,ko wadda ma ba musulmar ba,da zata shigo garin Kano da sunan a bata suturar fitsaranci,domin ta bayyana surarta,a sanya mata waka da kida tana rawa,mai camera yana daukar hotonta da sunan sana'a,kuma har akai wannan abu gaban jami'an gwamnatin musulunci ta jihar Kano su amince da wannan abu ya shiga kasuwa da izinin gwamnatin musulunci ta jihar Kano, a halin akwai malamai a cikin hukumar da data bada izinin shigar da wannan kaset kasuwa. Haba al'ummar Muhammadur Rasulillah SAWA muji tsoron Allah SWT mu daina yaudarar kawunanmu da sunan addini, idan zamu yi musulunci muyi shi gaba daya kada muyi imani da wani bangare mu kafirce da wani bangare, idan mun yi haka uwarmu daya ubanmu daya da Bush mai antaya bama-bamai akan al'ummar Manzon Allah SAWA jarirai da yara, mata da tsofaffi a kasashen Iraki da Afganistan, kuma ina son in tunatar da ku Allah SWT ya la'anci Yahudu ne saboda Malamansu suna sauya hukuncin daya saukar musu kamar yadda malamanmu a yau suke halasta zalunci da fajirci matukar dai za a basu kujerun hajji da kwangiloli da 'yan milliyoyin Nairori.
A karshe ina kira ga al'ummar hausa Fulani da kabilun cikinmu wadanda suka dauki sana'ar fim din hausa sana'a a garesu da su rike wannan sana'ata su da hannu biyu kuma su sanya tsoron Allah SWT a cikin wannan sana'a tasu domin sana'a ce wadda zata kai su ga samun rahamar Allah SWT matukar sun riketa tsakaninsu da Allah SWT da nufin illimantar da al'umma addinin Allah SWT da kuma nusar da al'umma kyawawan dabi'un musulunci da kuma munanan dabi'u. Hakan zai tabbatu kawai ne idan masu wannan harka ta fina-finai sun ji tsoron Allah SWT kuma sun nemi illimi na wannan sana'a tasu a addinance sun san abin da musulunci ya amince suyi a wannan sana'a tasu da kuma abin da yake haramun kuma suka yi hakan da kyakkyawar niyya. Sannan matan da suke baro kyauyukansu da rigagensu da biranensu suke kwararowa garin Kano da sunan sun zo shiga harkar fina-finan hausa wannan ya dace ya zama tarihi, domin babu ta yadda musulunci zai yadda da wannan abu. Kuma wannan abu ne ya jawo 'yan mata 'yan fim suka mai da karuwanci sana'a domin basa gaban iyayensu kuma basa gaban muharramansu, dama sun zo Kano ne neman kudi. Wanda da ace a lokacin da suka zo garin Kano sun samu Malamai sun yi aikin daya rataya akansu da babu wanda zai sauke su bare ya basu masauki a shagonsa ko a gidan gwaurantarsa ya fake da cewa sana'a suka zo yi. Kuma Ibrahim Mandawari kana cikin wanda ya ingiza mata 'yan fim fadawa cikin muguwar hanya musamman ta hanyar shirinka na Fina-finan hausa da kake gabatarwa a gidan rediyon Freedom,a cikinsa kake fito da matakai na arziki da masu sana'ar fina-finai na hausa suke takawa wanda da kunne na naji kana lissafin matan da suka mallaki mota a hanyar fim, wanda hakan kana bude kofa ne ga mata su baro gidajen iyayensu ko auransu su fada harkar fim, wanda sai sun fada harkar sai su ga abin ba haka bane ba, idan suna son mallakar mota sai sun bi ta hannun kawalai sun hada su da fasikai. Kuma ina fatan Ibrahim Mandawari ba zaka manta da abin da ka fada kai da 'yan uwanka masu fim a ranar lahadin da ka gabatar da shirin "Dan Kuka Mai Jawo Uwarsa..." wanda kayi akan abin rashin dadin daya faru na Maryam Hiyana a gidan rediyon Freedom inda da bakinka kai da sauran 'yan fim da ka gayyato kuka ce babu ta yanda za ayi mace ta mallaki mota a sana'ar fim a halin irinsu na Kwango da Sule Koki basu mallaka ba idan dai har da kudin da ake biyan ta ne.
A karshe Malamai dana batawa rai akan abin dana fada na gaskiya bana bukatar su yi hakuri, bukata ta kawai shine su bi hanyar shiriya su tserar da al'umma. Sannan 'yan fim din hausa musamman mata kar ku dauka ina mara muku baya ne, a'a, ni ina fadar gaskiya ne wadda ko ta kare ce ya dace a bashi kayarsa. Ni bana goyon bayan waka da rawa da muguwar shiga da kuke yi a fina-finan hausa, domin wannan ya sabawa addini na da al'ada ta, kuma ina bakin ciki da halin da malamai suka jefa ku a ciki har kuka samu kan ku a cikin wannan muguwar hanya, domin da malamai sun illimantar da al'umma kuma sun wa'azantar da al'umma da baku samu kanku a wannan muguwar hanya ba, Allah ya saka muku a bisa zaluncin da malamai suka yi muku, suka bar ku kuka fada muguwar hanya wanda da sun yi aiki da illiminsu wallahi da dukkan ku kuna gidajen mazajenku kuna cin ribar rayuwarku ta hanyar kyautatawa mazajen ku, ku sanya musu kananan kaya a baku lada, ku musu girki mai dadi a baku lada, ku yi hira dasu a baku lada, ku yi musu magana mai dadi a baku lada. Amma gashi sun zalunce ku sun barku cikin kaskanci da shaye shaye da muguwar makoma a gobe kiyama.
DAGA:
RABIU HAMDALA KANO,
08065273401.